Adamawa: An Cafke Mutumin Da Ya Kashe Wanda Ya Maye Gurbinshi A Ofis

An kama wani matashi mai suna Iliyasu Suleiman, bisa zargin kashe wani mutum da aka dauke shi aiki don ma ye gurbinsa bayan an kore shi daga kamfanin da ya yi aiki kan zargin sata a jihar Adamawa.

Mutumin mai shekaru 40, wanda ake zargi daga gundumar Ngurore da ke jihar Adamawa, kamfanin sabis ne ya dauke shi aiki a matsayin mai gadi a shekarar 2020, kuma an kore shi daga aiki a watan Yulin 2021 bayan an zarge shi da satar kadarorin kamfanin.

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Suleiman Nguroje, ya bayar a ranar Litinin, wanda ya tabbatar da kamun nasa, ya ce wanda ake zargin ya furta cewa ya buge sabon jami’in tsaron sabis din.

Suleiman ya yi ikirarin cewa ya sace sandar ?arfe na kamfanin ya sayar da shi ga wani mai sa?a a kan N5, OOO, bayan haka kamfanin ya kai ?ararsa ga ‘yan sanda da suka binciki lamarin tare da gano sandunan ?arfen.

Ya ce duk da mahukuntan kamfanin sun yi barazanar korar sa, amma an ba shi damar ci gaba da zama bayan ya roke su, kuma ya yi aiki a kamfanin na tsawon shekara guda.

Koyaya, bayan an yi masa afuwa kuma ya ci gaba da aiki, makonni ka?an bayan haka, wasu mutane suna satar abubuwa a inda kamfanin ya dage cewa dole ne ya zama mai alhakin hakan ya kuma haifar da korarsa ta ?arshe daga kamfanin a cikin Yuli 2021.

Related posts

Leave a Comment