Labarin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar tsohon gwamnan jihar Jigawa Sule Lami?o ya ce a yanzu da ‘yan Najeriya na kallon jam’iyyar PDP a matsayin fata daya tilo a garesu da za ta ceto su daga halin da suke ciki.
Da yake magana yayin wani shiri a gidan Talabijin na Channels, a ranar Lahadi, tsohon gwamnan ya ce shirye-shiryen da jam’iyyar ke ci gaba da yi dangane da babban zaben 2023 na ganin amfani da ci gaban kasa ne.
Ya ce neman goyon baya da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP ke yi a fadin kasar nan zai kara daukaka martabar jam’iyyar.
“A PDP, duk abin da za mu yi don amfanin Najeriya shi muke yi, ba na mu ba. Jama’a na ganin PDP ce kawai fata a Najeriya a yau. “Muna duba abin da muka fito da shi kuma ‘yan Najeriya za su ji dadin hakan kuma za su ba su yanayin da zai dawo da kaunar juna da aminci tsakanin juna.
“A gare ni, kafin ku yi wani abu, muna bukatar mu maido da amana a tsakaninmu. “A bayyane yake, a Najeriya a yau, ba mu amince da juna ba. Ba mu jin yarda da junanmu yanzu. Hadin gwiwarmu babu ita a yanzu. Dangantakarmu daya ita ce dan adamtaka.”
