2023: APC Ta Dage Ranar Tantance ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Jam’iyyar APC mai mulki ta sanar da ?age ranar tantance masu takarar shugabancin kasa a karkashin jam’iyyar.

Tun da farko jam’iyyar ta sanya tantancewar ta kasance a ranar Litinin, 23 ga watan Mayu na shekarar 2022.

An ruwaito cewa, jam’iyyar mai mulki za ta bayyana sabuwar ranar da za ta tantance ‘yan takarar nan gaba kadan.

Related posts

Leave a Comment