Tinubu Ya Roki Buhari Ya Dauki Matasa Miliyan 50 Aikin Soja

Jagoran jam’iyya mai mulkin ?asar nan (APC) Bola Tinubu,ya kirayi gwamnatin tarayya da ta ?auki matasa miliyan 50 aikin soja don magance matsalar tsaro data addabi ?asar.

A jawabin da ya yi a wajen taron bikin murnar cikarsa shekaru 69 a duniya, Tinubu yace ?aukar wannan matakin zai kara taimakawa wajen ya?i da ta’addanci.

“Muna ?arkashin ‘yan sanda kuma muna fama da matsalar ‘yan fashi da makami, da ‘yan bindiga. A ?auki matasa masu ?anyen jini a jiki aikin soja kamar mutum miliyan 50 domin shawo kan matsalar.

“Ku daina cewa jahilci ke damun su, duk mutumin da zai iya ri?e bindiga, zai iya sarrafa ta, kuma zai iya shiryawa ya yi harbi da ita to wannan zai iya gyara babbar mota a gareji.”

Tsohon gwamnan jihar Lagos ?in ya jinjina ma matasa musamman wa?anda suke nuna a shirye suke wajen taimakawa a dawo da zaman lafiya a ?asar nan.

Taron wanda ya gudana a jihar Kano anyi masa take da: “Hadin kan mu, arzikin mu: Wajibi ne ga hadin kan kasa don girma da ci gaba”.

Related posts

Leave a Comment