Shuugaba Bola Tinubu ya tabbatar wa ?an Najeriya cewa gwamnatinsa za ta shawo kan matsalar ta?ar?arewar tattalin arziki da kasar ke fama da shi, ciki har da sauko da hauhawar farashin kayayyaki.
Ya ce duk da cewa shi ba na daban bane, amma kada ‘yan Najeriya su damu saboda yana da zimmar kawo karshen hauhawar farashi.
Tinubu ya bayyana haka ne lokacin da ya kar?i bakuncin kwamitin ya?in neman za?en jam’iyyar APC a wajen bu?e-baki a fadarsa da ke Abuja ranar Laraba, inda ya ce gwamnatinsa na aiki tukuru don sauko da farashin kayayyaki.
“Wannan alkawari ne mai wahala da kuka yi wa al’ummar Najeriya lokacin da kuke min yakin neman za?e, dole ne na yi aiki don tabbatar da haka.
“Na yi kamfe kan fata mai kyau, dole ne na ?abbaka wannan fata da kuma fatan ganin kowaye cikinmu ya ji da?i. Tattalin arzikinmu na kan turba mai kyau. Kada ku damu kan haka,” in ji Tinubu.
Ya ce Najeriya na fama da matsalar hauhawar farashi kuma a shirye gwamnatinsa take wajen magance ta.
“Muna sake fasalin harkokin ku?ir shigarmu, kuma muna samun nasara kan haka, kuma muna dawo da tagomashinmu a fa?in duniya,” in ji shugaban Najeriyar.
