Labarin dake shigo mana daga Jihar Katsina na bayyana cewa wasu gungun ‘yan bindiga sun yi awon gaba da mutum hudu cikin su har da surukar Sanata mai wakiltar maza?ar Katsina ta arewa a majalisar Dattawa, Sanata Ahmed Babba Kaita.
Wani mazaunin garin Kankia, Malam Muhammad Sani, ya ce maharan sun farmaki garin ne a farkon awannin ranar Litinin kuma suka ci karen su babu babbaka na tsawon awanni.
Ya ce faramakin ya faru ne a Anguwar Bakin Kasuwa, inda yan bindigan suka kutsa kai gidan Mani Babba Kaita, ?anin Sanata Ahmed Babba Kaita, suka yi awon gaba da matarsa.
Ya ?ara da cewa maharan sun kuma shiga gidan wani Sabe Halilu a wannan Anguwa, inda suka ci zarafin matarsa kana suka sace ?a?ansa biyu, cikin su har da ?alibar Firamare.
Wani mazaunin Kankia na daban, Salisu Musa, ya ce maharan sun sace wata matar aure duk a wannan Anguwa ta Bakin Kasuwa. Mutumin ya ce: “Gaskiya sun zo ne da nufin sace ?an uwan Sanatan, amma ya fice daga gidan.
?aya daga cikin matansa ta tsira, amma wacce abun ya shafa ta ga ba zata iya guduwa ta bar ?a?anta ba, shiyasa suka same ta.”
“?ayar matar kuma mijinta baya nan lokacin da suka zo, yayin da ta yi nufin guduwa sai maharan sun cafko ta suka laka?a mata duka, suka ha?a da ‘ya’ya biyu. A baki ?aya harin, sun sace matan aure biyu da kananan yara biyu.”
