Labarin dake shigo mana daga Fadar Shugaban ?asa dake Abuja na bayyana cewar, Shugaba Muhammadu Buhari ya isa birnin Paris na Faransa, a wata ziyara ta kwana ?aya, kamar yadda wata sanarwa daga fadarsa ta bayyana.
Mai taimaka wa shugaban kan ya?a labarai Femi Adesina a sanarwar ya ce shugaban ya kai ziyarar ne bisa gayyatar da Shugaba Emmanuel Macron ya yi masa.
Buhari dai ya yi ?aurin suna wajen yawan yin tafiye-tafiye zuwa kasashen waje, lamarin da jama’ar ?asar da dama ke ?orafi akai.
