Site icon Muryar 'Yanci

Tinubu Ya Dawo Najeriya Daga Faransa

Rahotanni daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC mai mulki Asiwaju Bola Tinubu, ya dawo Najeriya daga kasar Faransa.

Tinubu ya bayyana haka a shafin sa na Tuwita, da Instagram a lokacin da jirgin nasa ya sauka Najeriya da yammacin ranar Asabar.

Tinubu ya bar Najeriya ne jim kadan bayan ya yi wata ganawar sirri da shugaban kasa Muhammadu Buhari a fadar shugaban kasa da ke Abuja, a ranar 27 ga watan Yuni.

Exit mobile version