Jami’an soji a Burkina Faso da Nijar sun ce an kashe ?an bindiga da dama masu daawar jihadi a wani samamen ha?in gwiwa da aka ?addamar a iyakokin ?asashen biyu.
Kamfanin dillacin labaran AFP ya ruwaito wata sanarwa da ta ce an kashe maya?a kusan 100 a farmakin na mako biyu da ya ?unshi ?aruruwan sojoji.
Rahotannin sun ce an kwace makamai, da bama-bamai da aka kera a gida da kuma babura sama da 100.
Mayakan masu daawar jihadi da ke addabar ?auyukan ?asashen biyu da na Mali – galibi suna amfani da babura ne yayin kai hare-hare.
A farkon watan Yuni sama da mutane 170 aka kashe a wasu kauyuka biyu da ke arewa maso gabashin Burkina Faso – hari mafi muni a cikin shekaru.
Gwamnati ta zargi masu daawar jihadi – wasu daga cikinsu ta ce yara ne ?an shekara 12.

