Site icon Muryar 'Yanci

Siyasa: Pantami Ya Shirya Wa Kayode Walima

Ministan harkokin Sadarwa Sheikh Isa Pantami ya shiryawa sabon dan jam’iyyar APC Chief Femi Fani-Kayode liyafar cin abinci a gidansa.

A cewar Mista Fani-Kayode, ministan ya gayyace shi, shi da Gwamnan Zamfara Bello Matawalle.

“Ni da abokina kuma dan uwana Gwamna Bello Matawalle, mun ji dadin karamci and girmamawa da gayyatar liyafar cin abinci da abokina kuma dan uwana ministan Sadarwa Farfesa Isa Pantami ya gayyace mu a daren jiya, a gidansa na alfarma,” a cewar Mista Fani-Kayode a shafinsa na Facebook.

Ya ce sai da su ka raba dare su na hira kan al’amuran kasa da na waje.

Exit mobile version