Site icon Muryar 'Yanci

Neja: Hukumar Wutar Lantarki Ta Yanke Wutar Gidan Gwamna

Labarin dake shigo mana daga Minna babban birnin jihar Neja na bayyana cewar Kamfanin Abuja Electricity Distribution Company watau AEDC masu raba wutar lantarki a jihar sun datse wutar gidan Gwamnati da ma’aikatun gwamnati.

Hakan ya biyo bayan tulin bashi da kamfanin na AEDC yake bin gidan gwamnati, ma’aikatu da hukumomin jihar ta Neja. AEDC sun ba gwamnatin Neja wa’adi ta biya kudin, da abin ya gagara sai aka yanke masu wuta.

Kamar yadda jami’in hulda da jama’a na kamfanin AEDC, Mohammed Pele ya shaidawa ‘yan jarida a ranar Juma’a, kudin da suke bi ya kai N1.3bn.

Mohammed Pele yace baya ga ma’aikatun gwamnatin Neja, kamfanin ya yanke wutar lantarki a gidan gwamnati da asibitin da ke fadar gwamna.

Pele yace kwanakin baya majalisar dokokin Neja ta sa baki a maganar bashin, har aka amince gwamnati za ta biya kamfanin 80% na kudin da suke bi.

Tun da aka yi wannan magana da ‘yan majalisar jihar, jami’in yada labarai na kamfanin yace gwamnatin Neja ba ta biya su ba, wanda hakan ya sanya dole aka datse su.

Exit mobile version