Site icon Muryar 'Yanci

NEJA: Dakarun Soji Sun Hallaka Tarin ‘Yan Bindiga

Labarin dake shigo mana daga Minna babban birnin Jihar Neja na bayyana cewar rundunar Sojan Sama ta ?asa ta ce dakarunta sun yi nasarar kashe tarin ‘yan bindiga a Jihar Neja.

Sanawar da rundunar ta fitar ta ce a ranakun karshen makon nan ta kai harin a kan Aminu Duniya lokacin da yake jagorantar wani taro da mayakan kungiyar a garin Kurebe na Karamar Hulkumar Shiroro.

“Sai dai babu tabbas ko shi ma Aminu Duniya ya mutu a harin,” a cewar sanarwar.

“Yayin da sojojin kasa suka toshe hanyoyin yankin, jirgin sojin sama ya bude wuta a inda ‘yan ta’addan suke…kuma an tabbatar da mutuwar ‘yan ta’addan masu yawa.”

Exit mobile version