Site icon Muryar 'Yanci

Ministan Yada Labarai Ya Soki Lamirin Tiwita

Ministan yada labarai na Alhaji Lai Muhammad ya caccaki Twitter tare da zargin kamfanin da zama mai fuska biyu.

Cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, Alhaji Lai ya ce, ya yi wannan zargin ne biyo bayan zanga-zangar masu manyan motoci da ke faruwa a Canada saboda dokar hana zirga-zirga da aka sanya dalilin annobar korona, wanda hakan ya kawo tsaikon kasuwanci da Amurka.

Masu zanga-zangar sun toshe manyan titunan birnin Ontario, wanda hakan ya janyo bacin rai ga kamfanoni da kuma daidaikun mutane har ma da gwamnati.

Gwamnatin kasar ta bayyanasu a matsayin ” ‘yan ta’adda ko kuma wadanda suke rikici da gwamnati”.

Kamfanin asusun da ke tara kudi ya rufe asusun masu zanga-zangar bayan sun tara dala miliyan 10, haka shi ma Twitter ya dakatar da shafinsu yayin da gwamnatin Ontario ta kulle asusunsu mai dauke da miliyoyin kudi da suka tara a intanet.

Sai dai duk ya fa?i wadannan hujjoji ne domin tuna baya lokacin zanga-zangar EndSars, da kasancewar Canada a matsayin daya daga cikin kasashen da suka nuna goyon bayansu ga masu zanga-zangar.#

Da kuma matakin da Twitter ya dauka ya dauka na goge sakon shugaba Buhari da taimaka musu wajen tattara kudade da za a yi amfani da su.

Exit mobile version