Site icon Muryar 'Yanci

Matsalar Tsaro: Rashin Sanin Makaman Mulki Ya Kai Gwamnonin Arewa Amurka – Lamido

IMG 20240429 WA0026

Tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido, ya soki gwamnonin Arewa kan tafiyar da suka yi Zuwa ?asar Amurka.

Sule Lamido ya bayyana ra’ayinsa a wani sakon da ya wallafa a Facebook, inda ya bayyana cewa tafiyar ta nuna Rashin fahimtar tsarin mulkin kasar da gwamnonin suka yi.

Ya kuma jaddada cewa, tsaro yana ?ar?ashin gwamnatin tarayya ne kawai, domin yana cikin ajandar zartarwa da majalisar dokoki.

Sule Lamido yayi nuni da rashin alaka tsakanin ayyukan gwamnoni da ayyukan da kundin tsarin mulki ya dora musu. Ya soki matakin da suka dauka na shiga tattaunawa da suka shafi tsaro, wanda ke karkashin jerin ‘yan majalisar dokoki na musamman, maimakon mayar da hankali kan batutuwan da suka shafi yankinsu, kamar noma ko kiwon lafiya.

Lamido ya yi nuni da matsaloli daban-daban na cikin gida da ke bukatar kulawa, kamar rashin tsaftataccen ruwan sha, Da rashin ingantaccen ilimi. Ya kara da cewa Wadannan batutuwa na haifar da babbar matsala ta tsaro da gwamnonin suka kasa magancewa.

Bugu da kari, Lamido yayi Allah wadai da yadda wasu gwamnoni ke nuna kyama ga dukiyar ?asa da kuma rashin mutunta mutuncin ‘yan kasa, Wanda ke ?ara ta’azzara talauci da Rashin tsaro.

Ya bada shawarar cewa idan da gaske gwamnonin za su magance matsalolin tsaro, da sun yi amfani da cibiyoyin gida kamar su NIPSS a Kuru Jos, ASCON a Badagry, ko NIA, maimakon tafiya Amurka mai tsada da almubazzaranci. Wadannan cibiyoyi, a cewar Lamido, suna da isassun kwarewa da kayan aiki don magance matsalolin tsaro a Najeriya yadda ya kamata.

Exit mobile version