Site icon Muryar 'Yanci

Matsalar Tsaro: Buhari Ya Tura Dakarun Soji 100 Zamfara

Rahotanni daga Gusau babban birnin Jihar Zamfara na bayyana cewar Gwamnan jihar Bello Matawalle ya yaba wa Shugaba Muhammadu Buhari kan bayar da umarnin aika Dakarun kar ta kwana na musamman don yaki da ‘yan bindiga a jihar.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a yau Alhamis lokacin da ya karbi baukuncin babban kwamandan runduna ta takwas da sojin Najeriya da ke Sokoto da kwamandan rundunar hadin gwiwa na yankin arewa maso yammacin kasar na rundunar Hadarin Kaji.

Gwamnan y ace ya ji dadin aike wa da dakaru na musamman har 100 da shugaban kasa ya yi jihar Zamfara, yana mai cewa matakin zai kawo karshen ta’addancin da ake yi a jihar.

Ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da bai wa rundunar sojin Najeriya dukkan hadin kan da take bukata don magance matsalar rashin tsaro.

Exit mobile version