Majalisar ?inkin Duniya ta yi tir da harin ranar 24 ga watan Janairu da sojojin Najeriya suka kai kan wasu Fulani makiyaya a Jihar Nasarawa da ke tsakiyar Najeriya.
Harin ya yi sanadiyyar kashe mutum a?alla 40, a cewar MDD.
Mai bai wa MDD shawara ta musamman kan kare kisan ?are-dangi, Alice Nderitu, ita ce ta yi wadai da kisan, tana mai bayyana damuwa game da ?aruwar hare-hare a arewa maso yamma da kuma tsakiyar Najeriyar.
“Irin wannan hare-hare a kan mutane kawai saboda ?abilarsu ka iya ta’azzara rikicin ?abilanci, da shiga ?ungiyoyin ‘yan bindiga, da hare-haren ramuwar gayya, wanda zai dinga ?arewa a kan fararen hula,” in ji ta.

