Site icon Muryar 'Yanci

Majalisar Dattawa Ta Zabi Jagororin Majalisa

Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Godswill Akpabio ya sanar da manyan Majalisar ta 10 a jam’iyyarsu ta APC – ?angaren masu rinjaye ke nan.

Haka nan ya sanar da na marasa rinjaye, wato na jam’iyyun adawa.

Ga yankunan da na masu rinjaye suka fito:

Sanata Opeyemi Bamidele – Shugaban Masu Rinjaye daga Jihar Ekiti (kudu maso yamma)
Sanata David Umahi – Mataimakin Shugaban Masu Rinjaye daga Jihar Ebonyi (kudu maso gabas)
Sanata Ali Ndume – Mai Tsawatarwa na Masu Rinjaye daga Jihar Borno (arewa maso gabas)
Sanata Lola Ashiru – Mataimakin Mai Tsawatarwa na Masu Rinjaye daga Jihar Kwara (arewa ta tsakiya)
Yankunan da na marasa rinjaye suka fito:

Sanata Simon Davou na PDP – Shugaban Marasa Rinjaye daga Jihar Filato (arewa ta tsakiya)
Sanata Oyewunmi Olarere na PDP – Mataimakin Shugaban Marasa Rinjaye daga Jihar Osun (kudu maso yamma)
Sanata Darlington Nwokeocha na LP – Mai Tsawatarwa na Marasa Rinjaye daga Jihar Abiya (kudu maso gabas)
Sanata Rufai Sani Hanga na NNPP – Mataimakin Mai Tsawatarwa na Marasa Rinjaye daga Jihar Kano (arewa maso yamma)

Exit mobile version