Rahotanni daga Jihar Kebbi na bayyana cewar wasu gungun yan bindiga sun yi garkuwa da dalibai masu yawa daga Kwalejin Tarayya da ke garin Yauri a jihar Kebbi.
Sashin Hausa na BBC ta ruwaito cewa shaidar gani da ido sun ce maharan sun yi awon gaba da dalibai da dama sannan suka harbi wasu daga cikinsu.
An tattaro cewa wani da abun ya faru a kan idonsa ya sanar da sashin labaran cewa ‘yan bindigar sun ci karfin ‘yan sandan da ke gadin makarantar sannan suka kwace motoci kirar Toyota Hilux daga wurinsu inda suka zuba daliban sannan suka tafi da su.
An kuma ruwaito cewa maharan wadanda suka kai wa makarantar hari a kan babura sun fito ne daga dajin Rijau da ke makwabtaka. Har ila yau, an bada rahoto cewa an kai dalibai da dama asibiti domin samun kulawar likitoci sakamakon raunukan da suka ji na harbi a yayin da suke tserewa daga harin na ‘yan bindiga.

