Site icon Muryar 'Yanci

Kano: An Nada Sabon Sarkin Masarautar Gaya

Rahotanni dake shigo mana daga Jihar Kano na bayyana cewar Gwamnan jihar Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya amince da nadin Alhaji Aliyu Ibrahim Gaya a matsayin sabon sarkin masarautar Gaya.

Wannan ya biyo bayan zabinsa da masu zaben Sarkin masarautar sukayi a jiya Asabar.

Sakataren Gwamnatin jihar, Usman Alhaji, ya bayar da wannan sanarwa a gidan gwamnatin jihar yayinda aka karbi bakuncin masu zaben Sarki.

A Laraba, 22 ga Satumba 2021, Allah ya yiwa Mai Martaba Sarkin Gaya , Alhaji Ibrahim AbdulKadir, rasuwa.

Wannan sanarwa ta fito ne daga bakin babban hadimin gwamnan Kano kan kafafen yada labaran zamani, Abubakar Aminu Ibrahim.

Exit mobile version