Site icon Muryar 'Yanci

Kaduna: ‘Yan Bindiga Sun Bindige Basaraken Dogon Daji

Wasu ‘yan bindiga sun kashe Dagacin Dogon Daji, Mallam Anja, da ke ?aramar Hukumar Sanga ta Jihar Kaduna a arewacin Najeriya.

“Yan bindigar da ake zargin ‘yan fashin daji ne sun kai wa gidan dagacin hari kuma suka harbe shi, abin da ya yi sanadiyyar mutuwarsa nan take, a cewar gwamnatin jihar.

Kwamishinan Tsaro na Kaduna, Samuel Aruwan, ya ce ana gudanar da bincike kan lamarin domin gano wa?anda suka aikata kisan.

Kwamishinan ya ce Gwmana Nasir El-Rufai ya bayyana alhininsa game da kisan kuma ya yi addu’ar Allah ya ji kan basaraken.

Kazalika, gwamnan ya mi?a ta’aziyyarsa ga iyalan mamacin da kuma al’ummar Dogo Daji.

Exit mobile version