Fitaccen Mawakin finafinan Hausa dake birnin Kano Hamisu Breaker, ya bayyana jin dadi da farin cikinshi dangane da yadda sana’ar waka ke kara daga darajar shi a duniya.
Breaker ya bayyana hakan ne a yayin wata tattaunawa da gidan rediyon BBC Hausa yayi dashi cikin shirin daga Bakin mai ita.
Sai dai mawakin ya koka dangane da yadda wasu jama’a ke mishi kallon yana Shaye-Shaye, lamarin da ya sanya har wasu ke kawo mishi kyaututtuka na kayan Shaye-Shaye.
Hamisu Breaker ya kuma musanta zargin da ake yi na cewar suna soyayya da Jarumar Hausa Fim Momi Gombe,inda ya bayyana ta matsayin abokiyar aiki amma ba wadda suke da soyayya ba.
Tauraron Mawakin dai ya fara haskawa ne a ‘yan shekarun baya biyo bayan wata wakarshi da ya yi mai suna “Gimbiyar Hausa” wakar da ta yi farin jini wurin jama’a musamman Mata.

