Shugaban ?asa Muhammadu Buhari a jiya Asabar yayin da yake sake jaddada kasancewar sa a jamiyyar APC yayin da yake ganawa da wasu daga cikin mukaraban sa a mahaifar sa ta Daura dake jihar Katsina.
Shugaba Buhari ya bayyana cewa yana nan daram a Jam’iyyar APC ba zai canja jam’iyya ba, kuma nan gaba mutane za su sha mamaki.
An hango Muhammadu Buhari tsakiyar taro tareda wasu jiga-jigan jamiyyar ta APC .
A wannan ganawa Shugaban Najeriya ,ya kalubalanci rawar siyasar wasu yan kasar dake ci gaba tareda kokarin mayar da hannun agogo baya a kokarin da gwamnatin sa ke yin a ceto Najeriya daga durkushewa a cewar Shugaba Buhari.

