Site icon Muryar 'Yanci

Gwamnoni Sun Amince Da Zabin Shettima Mataimakin Tinubu

Rahotanni daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Gwamnonin jam’iyyar APC mai mulki sun bayyana goyon bayansu ga Sanata Kashim Shettima a matsayin ?an takarar mataimakin shugaban ?asa a jam’iyyar a za?en 2023.

Gwamnonin sun bayyana goyon bayansu ne bayan sun gana da Buhari a Daura.

A ranar Lahadi ne ?an takarar shugaban ?asa Bola Tinubu ya sanar da tsohon gwamnan Borno Sanata Kashim Shettima a matsayin wanda zai masa takarar mataimaki.

Shugaban gwamnonin na APC Gwamnan jihar Kebbi Abubakar Atiku Bagudu da gwamnan Imo Hope Uzodimma wa?anda suka yi magana a madadin sauran gwamnonin sun ce da yawun bakinsu aka amince da Kashim a matsayin ?an takarar mataimakin shugaban ?asa.

Sun kuma yi al?awalin yin aiki domin tabbatar da jam’iyyarsu ta APC ta yi nasara a za?en 2023.

Exit mobile version