Site icon Muryar 'Yanci

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana ‘Yan Bindiga Matsayin ‘Yan Ta’adda

Rahotanni daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Gwamnatin tarayya karkashin jagorancin Shugaban kasa Muhammadu Buhari ta ayyana aikin ‘yan bindiga a matsayin aikin ta’addanci a hukumance, kamar yadda FIJ ta tattaro.

Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya kuma Ministan Shari’a Abubakar Malami ne ya bayyana hakan yayin da ya bayyana a shirin ‘Barka da Hantsi’ na gidan Talabijin na Najeriya (NTA) a ranar Talata.

Ya ce ofishinsa na aiki don duba hukuncin da kotu ta yanke wanda ya umarci gwamnati ta ayyana ‘yan bindiga a matsayin ‘yan ta’adda.

A ranar Laraba babbar Kotun Tarayya ta samu takardar, inda Malami ya sanya hannu a cikinsu.

Mai shari’a Taiwo Taiwo na babbar kotun tarayya da ke Abuja, ya amince da bukatar da gwamnatin tarayya na neman alanta ‘yan bindiga da ‘yan fashin daji a matsayin ‘yan ta’adda.

Exit mobile version