Rahotanni daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Gwamnatin tarayya karkashin jagorancin Shugaban kasa Muhammadu Buhari ta ayyana aikin yan bindiga a matsayin aikin taaddanci a hukumance, kamar yadda FIJ ta tattaro.
Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya kuma Ministan Sharia Abubakar Malami ne ya bayyana hakan yayin da ya bayyana a shirin Barka da Hantsi na gidan Talabijin na Najeriya (NTA) a ranar Talata.
Ya ce ofishinsa na aiki don duba hukuncin da kotu ta yanke wanda ya umarci gwamnati ta ayyana yan bindiga a matsayin yan taadda.
A ranar Laraba babbar Kotun Tarayya ta samu takardar, inda Malami ya sanya hannu a cikinsu.
Mai sharia Taiwo Taiwo na babbar kotun tarayya da ke Abuja, ya amince da bukatar da gwamnatin tarayya na neman alanta ‘yan bindiga da ‘yan fashin daji a matsayin yan taadda.

