Rahotanni daga birnin Maiduguri na Jihar Borno na bayyana cewar Gwamna Babagana Zulum ya dakatar da shugabannin gudanarwar kwalajen fasaha na Ramat Polytechinc a Maiduguri, na tsawon wata shida.
Zulum ya kasance dalibi a kwalajen tsakanin 1986 zuwa 1988.
A lokacin wata ziyarar bazata, gwamnan ya kadu da ganin ?angarori da dama na kwalajen a lalace, kusan makarantar ta mutu murus.
Gwamnan ya ziyarci makarantar da misalin 9 na safe kuma ya tarar da dakunan gwaje-gwajen dalibai ba sa aiki, duk azuzuwa sun yi yana.
Zulum ya umarci kwamishinan ilimi, Dr Babagana Mallumbe ya kar?e ragamar gudanar da makarantar.
Gwamnan ya yi tattaunawar sirri da manyan shugabannin makarantar.

