Site icon Muryar 'Yanci

Asusun Bada Lamuni (IMF) Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Najeriya

IMG 20240226 WA0252

Asusun bayar da lamuni na duniya (IMF) ya rage hasashen da ya yi a kan bun?asar tattalin arzikin Najeriya na 2024 zuwa kashi 3.1.

Wannan na ?unshe ne a cikin sabon rahoton asusun a kan tattalin arzikin duniya na watan Yulin 2024, wanda aka wallafa a ranar Talata.

IMF ya ce an samu wannan koma baya ne saboda rashin bun?asar tattalin arzikin a zangon farko na wannan shekarar.

A bisa sabon hasashen, an samu raguwar kashi 0.2 a bun?asar tattali arzikin Najeriya, wanda a baya aka yi hasashen zai tashi da kashi 3.3 cikin ?ari.

Amma IMF ta ce tattalin arzikin Najeriyar zaii bun?asa da kashi 3.0 a cikin 2025.

Dama dai hukumar ?ididdiga ta Najeriya ta fitar da wasu al?alumma da ke nuna cewa tattalin arzikin ?asar da ake samarwa a cikin gida zai ragu zuwa kashi 2.98, a zangon farko na 2024, daga kashi 3.46 da aka samu a zangon ?arshe na 2023.

Exit mobile version