Site icon Muryar 'Yanci

An Kalubalanci Tinubu Ya Bayyana Matsayinsa Kan Yaki Da Rashawa

Kungiyoyin fararen hula fiye da 30 ciki da cibiyar CISLAC dake fafutukar kare fararren hula da kuma sa ido a kan harkokin yaki da cin hanci da rashawa sun bayyana cewa kamata ya yi shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya fito kararra ya bayyana matsayinsa a game da mahimmancin aikin yaki da cin hanci da rashawa a kasar.

Jagoran kungiyoyin fararren hulan wanda shi ne shugaban cibiyar CISLAC kuma wakilin kungiyar Transparency International a Najeriya, Auwal Musa Rafsanjani ne ya bayyana matsayin da suka dauka na yin kiran a kan bukatar shugaba Tinubu ya fito kai tsaye ya bayyana matsayinsa a game da batun yaki da almundahana a kasar.

Barrister Mainasara Kogo, fitaccen masanin kundin tsarin mulki a kasar, ya ce tsarin mulki ya wajabtawa duk wani jami’in gwamnati a kan ya yaki cin hanci da rashawa.

A cikin shawarwarin da suka bai wa gwamnatin shugaba Tinubu, kungiyoyin sun bukaci a kaddamar da dokar kariya ga jami’an EFCC da ICPC da saura cibiyoyin yaki da almundahana, sai kuma kare masu kwarmata bayanai a kasar, sai batun yadda za a aiwatar da dabarun yaki da cin hanci da rashawa na kasa da dokar ‘yancin watsa labarai ta shekarar 2011 a duk jihohin tarayya ciki har da Abuja da dai sauransu.

Idan ana iya tunawa dai gwamnatin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ta hau mulki ne da manyan alkawura 3 ciki har da batun yaki da cin hanci da rashawa, sai dai masu ruwa da tsaki na ganin ba a cimma nasara a kan wannan kuduri ba.

Exit mobile version