Site icon Muryar 'Yanci

An Kakaba Sabon Harajin Kiran Waya Ga ‘Yan Najeriya

Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Gwamnatin tarayya ta kallafa sabon harajin kiran waya a kasar nan domin daukar nauyin kiwon lafiyar masu rauni a Najeriya.

An ruwaito cewa, wannan ya biyo baya yunkurin da kamfanonin sadarwa suka digan yi a cikin kwanakin nan na kara kudin kira sakamakon halin da suka tsinci kansu a kasar nan.

Harajin wayar na daidai da kwabo daya a duk dakika daya kuma yana daga cikin hanyoyin samun kudin da za a dauki nauyin kiwon lafiya na kyauta ga masu rauni a Najeriya.

Wannan na kunshe a sabuwar dokar Inshorar Kiwon lafiya ta 2021 da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya saka hannu a makon da ya gabata.

Dokar ta hada da tanadin sashi na 26, karamin sashi na 1c wanda ya ce inda za a samo kudin domin kungiyoyi masu raunin ya hada da harajin sadarwa wanda bai gaza kwabo daya ba a kowacce dakika na kiran waya.

Exit mobile version