Site icon Muryar 'Yanci

Adamawa: An Yi Kiran Manoma Da Makiyaya Su Rungumi Juna

An kirayi manoma da makiyaya da su kasance masu hada kansu da kuma kai zuciya nesa domin kaucewa tashin hankali a tsakanin manoma da makiyaya a fadin jahar Adamawa baki daya.

Kwamishinan yan sandan jahar Adamawa CP Aliyu Adamu ne yayi wannan kira alokacin yake tattaunawa da kungiyoyin manoma da makiyaya a yayinda ya ziyarci karamar hukumar Hong a jahar Adamawa.

Kwamishinan a wata sanarwa dauke da sanya hanun kakakin rundunan yan sanda a jahar Adamawa D S P Suleiman Yahaya Nguroje yace ya dauki matakin haka ne domin ganin ba a samu tashi hankaliba a tsakanin makiyaya da manoma.

Don haka nema ya shawarci manoma da makiyaya da koda yaushe su kasance masu neman zamàn lafiya domin samun cigaba a jahar dama kasa baki daya.

Shima a jawabinsa shugaban karamar hukumar Hong James Pukuma ya yabawa kwamishinan yan sadan bisa wannan majin kokari da yayi na hada kan manoma da makiyaya wanda a cewarsa hakan zai taimaka wajen Samar da zaman lafiya a tsakanin manoma da makiyaya.

Harwayau kwamishinan ya gargadi jami an tsaro dacewa duk wanda aka samu da hanu cikin duk wani karya dokan aiki to yayi kuka da kansa.

Exit mobile version