Rahotanni daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Mata da matasa da dama a fadin jihohin arewa 19, a ranar Jumaa, sun yi tururuwa a Abuja domin marawa jagoran jamiyyar APC na kasa, Asiwaju Bola Tinubu baya.
Sun nemi a tsayar da Tinubu a matsayin dan takarar jamiyyar mai mulki a zaben shugaban kasa mai zuwa, domin ?orawa daga inda Buhari ya tsaya.
Har ila yau, sun bayyana cewa Tinubu ne mutum daya tilo da ya cancanta kuma zai iya a cikin dukkanin masu takarar da suka ayyana kudirinsu na son daidaita tattalin arzikin kasar.
Karkashin jagorancin Yakubu Dauda, sun bayyana cewa matasa da matan APC a jihohin arewa 19 sun kasance dumu-dumu a harkokin jamiyyar ta hanyoyi daban-daban wanda ya karfafa jamiyyar a zukatan mutane.
Muna fatan sanar da shugaban kasa cewa muna ta tattarawa jamiyyar magoya baya a dukkan matakai a fadin jihohin arewa 19 yayin da ake shirye-shiryen zaben 2023.
Irin karbuwar da Tinubu ya samu a tsakanin talakawa abu ne mai ban mamaki za a iya tunanin cewa daga yankin arewa ya fito. A matsayinmu na gagarumar kungiya a cikin matasa da mata a jihohin arewa 19, ciki harda babbar birnin tarayya, muna iya fadi ba tare da tsoro ba cewa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya samu karbuwa sosai a matsayin babban dan takarar jamiyyarmu mai albarka a babban zaben 2023 mai zuwa.

